Hukumar ta ICPC da kan yaki cin hanci a tsakanin jami'an gwamnati ta sha alwashin sakamakon taron ba zai zama zane kan ruwa ba.
Sabon shugaban hukumar alhazan Najeriya ta NAHCON Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, ya yi alwashin yin tsayin daka a aikinsa bayan da aka bashi mukamin shuugabancin hukumar zan wajen sauke nauyin da a ka dora ma sa.
NLC ta ce wannan tamkar cin amanar yarjejeniyar karin mafi karancin albashi ne zuwa Naira 70,000.
Ganin yadda a wasu wurare zanga zangar da ake ta hada da kada tutocin Rasha, kwararru sun fara kallon zanga zanga ta wasu sabbin fuskoki, a yayin da su kuma hukumomi ke kokarin sanin abin da hakan ke nufi.
Masu sharhi kan lamuran yau da kullum da kuma wasu shugabannin al’umma na bayyana ra’ayoyi mabambanta kan shirin zanga-zanga da matasan Najeriya ke yi don nuna damuwa kan tsadar rayuwa da ake fuskanta a kasar.
Batun halalci ko haram na gudanar da zanga-zanga don kalubalantar salon mulkin shugabanni ya janyo sabanin fahimta tsakanin malaman addinin Islama a Najeriya.
Shugabannin kwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun kwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.
Barau Jibrin dai shi ya dau nauyin kudurin wanda Majalisar Dattawa da Wakilai suka amince da shi don kawo dauki ga magance kalubalen da ke addabar yankin na tsaro.
Alhazan duniya kimanin miliyan biyu na gudanar da tsayuwar Arfa a cikin tsananin zafin rana da ya kai ma’auni 46 na selso. Hakan ya sa bukatar alhazan su kaucewa yawan zirga-zirga a ranar don kare lafiyarsu.
A babban birnin Abuja ma'aikatu, da bankuna, da ma sauran sassa da su ka shafi gwamnati sun kasance a rufe.
A ranar Litinin din nan ne gamayyar kungiyoyin kwadagon Najeriya na NLC da TUC ke aukawa ckin wani gagarumin yajin aiki.
Hukumar yaki da cin hanci EFCC ta ce ta na sane da wani faifan bidiyo da a ka ga wani gwamna na watsa wa magoya bayansa kudi.
Hukumar kare hakkokin masu sayen kayayyaki ta Najeriya ta FCCPC na shirin rufe wani shagon ‘yan kasar China da ke Abuja, wanda rahotanni suka bayyana cewa yana nuna wariya ga 'yan Najeriya.
Iyayen 'yan matan Chibok sun bukaci a raba wasu daga cikin 'ya'yansu da a ka kubutar da tubabbun mazaje 'yan Boko Haram da ke zama da su a Borno karkashin kulawar gwamnati.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta fara nazarin rahoton babban mai bincike ayyukan Bankin CBN ya gudanar a zamanin mulkin Buhari.
'Yan kungiyar Shi'a almajiran Sheikh Ibrahim Elzazzaky sun gudanar da zanga-zangar marawa Falasdinawa baya kan yakin Gaza a sassa daban-daban na arewacin Najeriya.
Bisa yanda canjin dala ke hawa da sauka, hukumar alhazan Najeriya ta ce duk wanda zai biya kujera yanzu zai bada daga Naira 8, 254, 464 a arewa sai Naira miliyan 8, 454, 464 a kudu.
Gwamnatin Najeriya ta ayyana mawallafin jaridar DESERT HERALD Tukur Mamu a jerin mutanen da ta ke tuhuma da daukar nauyin ta'addanci a Najeriya.
Wata babbar kotun tarayya a Najeriya ta yi watsi da daukaka karar bukatar sako bayanan kadarorin tsofaffin shugabannin Najeriya, da suka hada da Goodluck Jonathan da Muhammadu Buhari da mataimakansu Namadi Sambo da Yemi Osinbajo.
Domin Kari