A wata sanarwa da ya fitar ta hannu kakakinsa Bayo Onanuga, Shugaba Bola Tinubu ya yi kira ga duk wanda bai gamsu da sakamakon zaben ba, ya bi hanyar da doka ta tanada don bin kadi.
Taron na bana za a gudanar da shi ne daga ranar 24 zuwa 28 ga Satumba, 2024 a birnin New York.
Najeriya ita ce ta shida a iya taka kwallo a nahiyar Afirka yayin da Libya take matsayi na 33.
Shugaban na Najeriya ya kuma yaba da yadda sauran ‘yan takara suka nuna dattaku yayin gudanar da zaben wanda ya ce an gudanar lami lafiya.
“Labarin Seaman Abbas Haruna mai cike da abin tausayi wanda aka nuna a shirin ‘Brekete’ ya sa kwamitin majalisar wakilai na sojin ruwan Najeriya ya shiga cikin lamarin da nufin bankado gaskiyar abin da ya faru."
Bidiyon ya nuna yadda matar Abbas Haruna mai suna Hussaina ta zayyana irin halin da mijinta ya shiga bayan da ya samu sabani da shugaban bataliyarsa lamarin da ta ce ya kai ga tsare shi har ma ya haukace.
Sai dai a wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar a ranar 15 ga watan Satumbar 2024, Ribadu ya nemi Aziegbemi da ya janye kalaman nasa inda ya kwatanta lamarin a matsayin “zuki ta malle”
'Yan takarar biyu sun yi musabaha a farko, suka tsaya a bayan mimbarinsu a wani dandamali a Cibiyar Kundin Tsarin Mulkin Kasa da ke Philadelphia, sannan suka fara caccakar juna.
Yankunan da ambaliyar ta shafa sun hada da Shehuri, wasu sassa na Yankin G.R.A., Gambomi, Budum, Bulabulin, Adamkolo, Wurin Millionaires, Kasuwar Litinin da Gwange a cewar hukumar ba da agajin ta gaggawa.
Najeriya tana jagorantar rukuni D da maki huɗu, yayin da Rwanda ke matsayi na biyu da maki biyu.
Tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso sun jajanta wa al’umar jihar Borno bisa ibtila’in ambaliyar ruwa da ta auka wa birnin Maiduguri da ke arewa maso gabashin Najeriya.
Kiyasi ya nuna mutum miliyan 51.3 ne suka kalli muhawarar Trump da Biden a watan Yuni, ana kuma hasashen wadanda za su kalli ta Trump da Harris za su haura wannan adadi.
A wata sanarwa da take fitarwa mako-mako, hukumar ta NCDC a rahotonta na mako na 35 ta ce an samu karin mutum biyar da cutar ta harba.
Rahotanni sun ce duk da an saki Ajaero, hukumar ta DSS ta kwace masa fasfo dinsa na tafiya.
Cikin wata sanawar da ta fitar, hukumar ta NEMA ta ce cikin makonni masu zuwa jihohin Benue, Kogi, Anambra, Delta, Imo, Rivers da Bayelsa za su iya fuskantar mamakon ruwan sama da ka iya haddasa ambaliyar ruwa.
Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta musanta ba kamfanin na NNPC umarnin ya kara farashin na litar mai.
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce za ta ba da tukwici mai tsoka ga duk wanda ya ba da bayanan da za su kai ga kama mutanen.
Domin Kari