Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

AFCON 2025: An Saka Ranar Karawar Najeriya Da Libya


Super Eagles (Hoto: Facebook/Super Eagles)
Super Eagles (Hoto: Facebook/Super Eagles)

Najeriya ita ce ta shida a iya taka kwallo a nahiyar Afirka yayin da Libya take matsayi na 33.

A hukumance, an fitar da ranakun da kungiyar ‘yan wasan Najeriya ta Super Eagles za ta kara da ta Libya a wasannin neman shiga gurbin gasar AFCON ta 2025.

Super Eagles za su karbi bakuncin wasan farko a ranar 11 ga Oktoba a birnin Uyo na jihar Akwa Ibom.

Kwanaki hudu bayan wannan karawa kungiyoyin za su sake haduwa a Tripoli.

Super Eagles ce ke jagorantar Rukunin D da maki hudu bayan nasara ta 3-0 a gida akan Benin da kuma canjaras da suka yi da Rwanda a Kigali.

Libya tana rike da matsayi na karshe a cikin rukunin tare da maki guda daga adadin wasanni biyu da ta buga.

Najeriya ita ce ta shida a iya taka kwallo a nahiyar Afirka yayin da Libya take matsayi na 33.

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG