Sanarwa ta kara da cewa, ana tuhumar Sonnberger, wacce 'yar kabilar Igbo ce da ke zaune a Canada da laifin furta kalamai na barazana.
A ranar Alhamis hukumar ta FIBA ta fitar da jerin sunayen kasashen.
A ranar Talata Amurka ta ba Najeriya allurar rigakafin cutar ta kyandar biri, hakan ya sa ta zama kasa ta farko a nahiyar Afirka da ta samu tallafin rigakafin.
Kungiyar ta NLC ta sha alwashin tsunduma yajin aikin da zai tsayar da al’amuran kasar cik idan har aka tsare Ajaero.
Omori ya ba da umarni a daukan bidiyon wakoki sama da 200 ciki har da na fitattun mawakan Najeriya irinsu Davido, Fire Boy da Ashake.
Fitar da sunayen ‘yan wasan na zuwa ne kwana guda bayan da aka nada Bruno Labbadio a mstayin sabon kocin kungiyar ta Super Eagles.
Rahoton na zuwa ne yayin da matsalar ambaliyar ruwa ta lalata amfanin gona da dama a wasu sassan kasar.
Yayin wannan ziyara, ana sa ran Tinubu zai gana da Shugaban China, Xi Jinping, inda za su rattaba hannu kan yarjeniyoyi masu muhimmanci a cewar fadar gwamnati.
Sai dai wannan sabuwar kiddiga da hukumar ta NBS ta fitar na zuwa ne yayin da ‘yan Najeriya ke fama da matsananciyar tsadar rayuwa, lamarin da ya kai ga gudanar da zanga-zanga a wasu sassan kasar a farkon watan Agusta.
Hukumar ta NFF ta sanar cewa ta cimma matsaya da Labbadia dan asalin kasar Jamus, wanda shi ne koci na 37 da zai horar da ‘yan wasan na Najeriya.
Wata sanarwa da kakakin Tinubu Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Litinin, ta ce Ambasada Mohammed Mohammed ne sabon shugaban hukumar ta NIA yayin da Mr. Adeola Oluwatosin Ajayi ya zama sabon Darekta-Janar na hukumar ta DSS.
Likitocin suna kira ne da a ceto Dr. Ganiyat Popoola wacce ‘yan bindiga suka yi garkuwa da ita a Kaduna sama da watannin takwas da suka gabata.
Taron a cewar wata sanarwa da hukumomin Saudiyya suka fitar a ranar Juma’a, za a yi shi ne tare da hadin gwiwar Kungiyar Hadin kan kasashen Musulmi ta OIC a ranar 26 ga watan Oktoban 2024.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Justice Kudirat Kekere-Ekun a matsayin sabuwar babbar mai shari’a ta Najeriya bayan da Babban Mai Shari'a Olukayode Ariwoola ya yi ritaya.
lamarin na faruwa ne yayin da ake ta ce-ce-ku-ce kan batun tallafin man fetur da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ce ta cire a bara, amma kuma wasu rahotanni ke zargin ana ci gaba da biyan kudin ta bayan fage.
Kudurin kwamatin shi ne a zartar da hukuncin da kotun koli ta yanke a ranar 11 ga watan Yulin bana na ‘yantar da kananan hukumomin daga jihohinsu.
“Sirrin da ke tattare da fannin man fetur din Najeriya da kuma rahotanni da ke cewa kamfanin mai NNPCL na biyan wasu kudade ta wata boyayyiyar hanya don a biya kudin tallafin man, na kara rikitar da mutane.”
Domin Kari