Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya Ta Tashi Canjaras Da Rwanda, Za Ta Hadu Da Libya A Watan Oktoba


Tawagar Super Eagles ta Najeriya
Tawagar Super Eagles ta Najeriya

Najeriya tana jagorantar rukuni D da maki huɗu, yayin da Rwanda ke matsayi na biyu da maki biyu.

Najeriya ta kasa doke Rwanda a wasan neman gurbin shiga gasar Kofin Nahiyar Afirka na 2025 da aka buga a Kigali ranar Talata.

An tashi wasan babu ci tsakanin kasashen biyu.

‘Yan wasan na Super Eagles ba su ji dadi, domin an hana su wata kwallo da suka ci a minti na 22.

Victor Boniface ya jefa kwallon ga Ademola Lookman wanda ya zura ta cikin raga, amma alkalin wasa ya hana domin satar gida Lookman ya yi.

Najeriya tana jagorantar rukuni D da maki huɗu, yayin da Rwanda ke matsayi na biyu da maki biyu.

A ranar Asabar Najeriya ta doke Benin a birnin Uyo da ci 3-0.

A watan Oktoba Najeriya za ta kara da Libya a wasanta na gaba.

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG