Majalisar Dattawan Najeriya ta umurci kwamitin ta da ke kula da harkokin shari'a, da yancin ‘dan Adam da na dokoki, da ya yi magana da ofishin Atoni Janar na kasa domin gudanar da bitar dokokin kasar tun daga shekara 2004 zuwa 2023, wadanda aka riga aka rattaba ma hannu domin a sa su a kundi guda.