Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ajaero Ya Amsa Gayyatar ‘Yan sanda, Ya Dawo Lafiya - NLC


Shugaban NLC, Comrade Joe Ajaero, (tsakiya,) sanye da bakar riga, bayan da ya dawo daga amsa gayyatar 'yan sanda (Hoto: Facebook/NLC)
Shugaban NLC, Comrade Joe Ajaero, (tsakiya,) sanye da bakar riga, bayan da ya dawo daga amsa gayyatar 'yan sanda (Hoto: Facebook/NLC)

Kungiyar ta NLC ta sha alwashin tsunduma yajin aikin da zai tsayar da al’amuran kasar cik idan har aka tsare Ajaero.

Shugaban Kungiyar Kwadago ta NLC a Najeriya, Joe Ajaero ya amsa gayyatar da ‘yan sanda suka aika masa a ranar Alhamis a Abuja, babban birnin kasar.

A makon da ya gabata jami’an ‘yan sandan Abuja suka aika wa Ajaero wasikar gayyata kan zarginsa da sa hannu a ayyukan ta’adanci da laifukan yanar gizo, zargin da Ajaero da NLC suka musanta.

Da misalin karfe 10 na safe Ajaero, wanda ya samu rakiyar fitaccen lauya, Femi Falana da dan fafutukar kare hakkin bil Adama Deju Adeyanju, ya bar hedkwatar kungiyar ta NLC don amsa gayyatar.

Mambobin kungiyar ta NLC sun yi dandazo a hedkwatarsu inda suka yi ta rera wakokin nuna goyon baya ga shugabansu.

Kungiyar ta NLC ta sha alwashin tsunduma yajin aikin da zai tsayar da al’amuran kasar cik idan har aka tsare Ajaero.

Sai dai daga baya kungiyar ta NLC ta tabbatar da dawowarsa bayan da ya amsa gayyatar ‘yan sandan a ofishinsu na Abbatoir da ke mahadar Guzape a Abuja.

“Shugabanmu ya amsa gayyatar, ya kuma dawo. Mun kuma fada musu ba mu da wani abu da muke boye wa.” In ji Sakatare-Janar na kungiyar ta NLC, Emmanuel Ugboaja yayin da yake jawabi ga mambobin kungiyar.

Tun da misalin karfe 8 na safe shugabannin kungiyar ta NLC suka fara taruwa a ofishin na NLC.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG