Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu Ya Nada Sabbin Shugabannin DSS, NIA


Shugaba Tinubu
Shugaba Tinubu

Wata sanarwa da kakakin Tinubu Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Litinin, ta ce Ambasada Mohammed Mohammed ne sabon shugaban hukumar ta NIA yayin da Mr. Adeola Oluwatosin Ajayi ya zama sabon Darekta-Janar na hukumar ta DSS.

Shugaban Najeriya ya nada sabbin shugabannin da za su jagoranci hukumomin tattara bayanan sirri na NIA da hukumar 'yanasandan farin kaya ta DSS.

Wata sanarwa da kakakin Tinubu Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Litinin, ta ce Ambasada Mohammed Mohammed ne sabon shugaban hukumar ta NIA.

Kazalika an nada Mr. Adeola Oluwatosin Ajayi a matsayin sabon Darekta-Janar na hukumar ta DSS.

Mohammed zai maye gurbin Ahmed Rufa’i Abubakar wanda ya ajiye aikinsa a karshen makon da ya gabata.

Shi kuma Ajayi ya maye gurbin Yusuf Magaji Bichi wanda Buhari ya nada a shekarar 2018.

Wane ne Ambasada Mohammed Mohammed

Ambasada Mohammed ya kasance cikin ayyukan da suka shafi harkokin waje tun da ya fara aiki a hukumar ta NIA a shekarar 1995.

Ya rike mukamai da dama inda har ya kai mukamin Darekta, ya kuma zama shugaban ofishin jakadancin Najeriya a Libya.

Ya kammala karatunsa ne a Jami’ar Bayero da ke Kano a shekarar 1990, ya kuma yi aiki a Koriya ta Arewa, Pakistan, Sudan da kuma fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Wane Ne Mr. Adeola Ajayi

Mr. Adeola Ajayi ya rike mukamai da dama a hukumar ta DSS inda har ya kai mukamin Mataimakin Darekta-Janar a hukumar.

Ya rike mukamin Darekta a jihohin Bauchi, Enugu, Bayelsa, Rivers, da kuma Kogi

“Shugaba Tinubu na fatan sabbin shugabannin hukumomin za su yi aiki tukuru waje samar da sauyi a hukumomin biyu don a shawo kan matsalolin tsaro da ke addabar kasar ta hanyar hada kai da sauran takwarorin aikinsu na tsaro.” In ji Ngelale.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG