Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Adadin Wadanda Suka Kamu Da Cutar Kyandar Biri A Najeriya Ya Kai 48 – NCDC


Wani mutum yana wucewa ta gefen wani allo da ke gargadi kan cutar mpox a filin tashin jirage, ranar 26 ga watan Agusta, 2024.
Wani mutum yana wucewa ta gefen wani allo da ke gargadi kan cutar mpox a filin tashin jirage, ranar 26 ga watan Agusta, 2024.

A ranar Talata Amurka ta ba Najeriya allurar rigakafin cutar ta kyandar biri, hakan ya sa ta zama kasa ta farko a nahiyar Afirka da ta samu tallafin rigakafin.

Hukumar da ke yaki da yaduwar cututtuka ta NCDC A Najeriya ta ce yawan mutanen da suka kamu da cutar Kyandar Biri a kasar ya karu zuwa 48.

Hukumar ta NCDC ta bayyana hakan ne a ranar Alhamis a rahotanta na mako na 34.

NCDC na fitar da rahoto a kowane mako kan cutar ta mpox.

“A rahotonmu na mako na 34 (19-25 watan Agusta), an samu sabbin mutum 8 da cutar ta mpox ta harba a jihohi biyar.

“Hakan ya sa adadin ya haura zuwa 48 na mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar.” NCDC ta ce.

A mako na 33, adadin mutanen da suka kamu da cutar 40 ne.

A ranar Talata Amurka ta ba Najeriya allurar rigakafin cutar ta kyandar biri, hakan ya sa ta zama kasa ta farko a nahiyar Afirka da ta samu tallafin rigakafin.

“Allurar rigakain guda 10,000 za a raba su a jihohi biyar domin kare wadanda suke cikin hadarin kamuwar da cutar.

“Hukumar Lafiya ta Duniya WHO na aiki da sauran abokan hulda don ganin an kara fadada raba allurar rigakafin a sassan Afirka.” WHO ta ce.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG