Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Masu zanga-zanga sun mamaye dandalin Tahrir da ke birnin al-Khahira


Masu zanga-zanga a Misra
Masu zanga-zanga a Misra

Dubun dubatan ‘yan Misra sun taru a dandalin Tahrir na birnin al-Khahira

Dubun dubatan ‘yan Misra sun taru a dandalin Tahrir na birnin al-Khahira a jiya Jumma’a inda su ka yi ta jaddada bukatarsu ta neman a kawo karshen mulkin soji duk ko da nada sabon Firayim Minista da gwamnatin mulkin sojin ta yi.

Yawan masu zanga-zangar ya yi ta karuwa a tsawon sati gudan da ya gabata, duk ko da jerin sauye-sauyen da gwamnatin ta sanar. A kalla mutane 41 ne aka kashe a tashe-tashen hankulan da ke da nasaba da zanga-zangar a fadin kasar.

Ana cigaba da tashe-tashen hankulan ne a sa’ilinda Misra ke shirye-shiryen fara zaben Majalisa a ranar Litini. Zaben zai kasance na farko tun bayan murabus din da tsohon shugaba Hosni Mubarak ya yi cikin watan Fabrairu sanadiyyar wata gagarumar zanga-zanga.

Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG