Ganin yadda talakawa su ka fara zanga-zangar nuna damuwa kan tsadar rayuwa a wasu yankunan Najeriya ya sa Majalissar Limamai da Malamai ta jihar Kaduna jawo hankalin gwamnati don kada a bar lamarin ya kazance.
Gobarar, da ta tashi cikin dare a kasuwar Panteka tsohowa dake cikin garin Kaduna, ta lakume rumfunan masu sayar da katako sama da hamsin kafin zuwan 'yan kwana-kwana wadanda su ka kashe ta.
Sama da kwanaki arba'in da harin jirgin sojan da su ka ce kuskure ne a garin Tudun Biri, wasu al’ummar yankin sun ce har yanzu gwamnati ba ta cika musu alkawurran da ta dauka ba.
Dukkan ‘yan majalisar dattawa 109 na Najeriya sun ce sun sadaukar da albashin su na wannan watan Disamba gaba daya ga iyalan wadanda su ka rasu sanadiyyar harin jirgin saman soji a garin Tudun Biri na jihar Kaduna.
Ganin yadda adadin wadanda su ka rasu sanadiyyar harin bam na jirgin sojan Najeriya yake karuwa bayan rasuwar wasu masu jinya, hadakar kungiyoyin matasa a Arewacin Najeriya sun gudanar da zanga-zangar nuna damuwa kan abin da ya faru a garin Tudun Biri na Karamar Hukumar Igabi ta jihar Kaduna.
Ana kara samun karuwar mutanen da su ka rasu biyo bayan harin kuskure na jirgin sojan kasan Najeriya kan masu taron Mauludi a garin Tudun Biri na Karamar hukumar Igabin jihar Kaduna, yayin da 'yan-uwa da iyalan wadanda abin ya shafa suka ce wasu masu jinya a asibiti sun kara rasuwa a ranar Talata.
Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da harin jirgin sama mara matuki da ya hallaka wasu masu taron Mauludi a garin Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi, sai dai ta ce kuskure aka samu kuma har yanzu ba a tantance adadin wadanda su ka rasu ba.
A yayin da takaddama kan sanadin mutuwar dalibin Makarantar Al-Azhar da ke Zariya ta barke tsakanin Makarantar da kuma iyayen dalibin, rundunar 'yan-sandan jihar Kaduna ta tabbatar da kama wasu mahukuntan Makarantar kuma ta ce bincike ya fara nisa.
Domin Kari