PNDS Tarayya Ta Musanta Zargin Hannun Tsohon Shugaba Issouhou Mahamadou A Juyin Mulki

Boubacar Sabo, sakataren harakokin zaben jam’iyar PNDS Tarayya ta Nijar

Jam’yar PNDS Tarayya madugar kawancen jam’iyun hambarariyar gwamnatin Nijar ta musanta zargin hannun tsohon Shugaban kasa Issouhou Mahamadou, a juyin mulkin da soja suka yi wa Mohamed Bazoum a ranar Larabar ta gabata.

NIAMEY, NIGER - A wata sanarwar da ta fitar a ranar Asabar uwar jam’iyar ta ce masu neman maida hannun agogo baya a yunkurin dorewar dimokradiya ne ke wannan ikirari da nufin dakile shirin sake mayar da shugaba Bazoum kan kujerar mulki.

Wannan bayani ne daga sakataren harakokin zaben jam’iyar PNDS Boubacar Sabo a lokacin da yake tanttaunawa da wakilin Muryar Amurka Souley Moumouni Barma a birnin Yamai.

Ga cikakken rahoto yadda hirar tasu ta kaya:

Your browser doesn’t support HTML5

Jam'iyar PNDS Ta Musanta Zargin Hannun Tsohon Shugaba Issouhou Mahamadou A Juyin Mulki .MP3