Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wani Hatsarin Jirgin Sama A Sudan Ta Kudu Ya Kashe Mutane 20


APTOPIX - Hatsarin Jirgin sama a Sudan ta Kudu
APTOPIX - Hatsarin Jirgin sama a Sudan ta Kudu

A yau Laraba ne wani karamin jirgin sama dauke da ma’aikatan hakar mai a jihar Unity ta Sudan ta Kudu yayi hatsari tare da hallaka mutane 20, a cewar hukumomi

Jirgin saman yayi hatsari ne a tashar jiragen sama ta Unity Oilfield da safiyar yau Laraba yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Juba, babban birnin kasar, kamar yadda ministan yada labaran kasar Gatwech Bipal ya bayyana.

Sudan ta Kudu
Sudan ta Kudu

Bipal yace fasinjojin jirgin ma’aikatan kamfanin hakar man hadaka na gpoc daya kunshi kamfanin man fetur na kasar China da takwaransa na “Nile Petroleum Corporation” mallakin Sudan ta Kudu.

Ya kara da cewar wadanda suka mutu a hatsarin sun hada da ‘yan China 2 da wani dan Indiya guda.

Bipal bai yi karin haske akan abinda ya sabbaba hatsarin ba.

Sudan ta Kudu
Sudan ta Kudu

Tunda fari kafafen yada labarai sun bayyana adadin wadanda suka mutu a hatsarin da mutum 18 saidai Bipal ya shaidawa Reuters cewar 2 daga cikin mutanen da suka tsallake rijiya da baya sun mutu daga bisani. Mutum guda ya rayu.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG