Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Mali Ya Ce Ya Tattauna Da Putin Game Da Juyin Mulkin Nijar


Shugaban sojojin Mali Assimi Goita
Shugaban sojojin Mali Assimi Goita

Shugaban sojojin Mali Assimi Goita ya fada a ranar Talata cewa ya tattauna ta wayar tarho da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin game da halin da ake ciki a Nijar, inda sojoji suka kwace mulki a wani juyin mulki a watan jiya. 

WASHINGTON, D.C. - Putin "ya jaddada mahimmancin warware matsalar cikin lumana don samun kwanciyar hankali a yankin Sahel," Goita ya ce a dandalin sada zumunta na X, wanda a da ake kira Twitter.

Shugaban Kasar Rasha Vladimir Putin
Shugaban Kasar Rasha Vladimir Putin

Kasashen yammacin duniya na fargabar cewa Nijar za ta iya fada wa irin halin da makwabciyarta Mali, wadda shugabanninta suka dauki hayar sojojin haya daga kungiyar Wagner ta Rasha domin taimaka musu wajen yakar ta da kayar baya, sakamakon hambarar da gwamnatin dimokaradiyya shekaru uku da suka wuce tare da korar sojojin Faransa.

Putin ya yi kira da a koma kan tsarin mulkin Nijar, yayin da shi kuma shugaban Wagner Yevgeny Prigozhin ya yi maraba da juyin mulkin.

Sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar
Sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar

Da alama goyon bayan Rasha na karuwa a Nijar tun bayan juyin mulkin ranar 26 ga watan Yuli, inda magoya bayan gwamnatin mulkin sojan kasar suka daga tutocin kasar Rasha a wasu taruka da dama.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG