Masu Fashi Da Makami Na Yiwa Mutanen Ghana Barazana

Mustapha Hamid wanda 'yan fashi da makami suka hallaka

Kasar Ghana ta soma fuskantar barazanar 'yan fashi da makami musamman a harabar bankuna da kamfanonin canji da sauran wuraren da ake hada-hada da kudi

An bayyana cewa kasar Ghana na fuskantar barazanar ‘yan fashi da makami musammam a birnin Accra da Tema inda har sakamakon irin wannan lamari yayi dalilin mutuwar wani dan taliki, Mustapha Hamid.

To sai dai duk da cewa jami'an tsaro na iya bakin kokarin su amma har yanzu da sauran rina a kaba, domin ko kawo yanzu ba mutun daya da aka samu nasarar kamawa kan aikata wannan danyen aiki.

Fashi da makamin da ya addabi biranen biyu ya fi aukuwa ne a harabar bankuna da wuraren da ake canji kudaden waje ko aika da kudi waje

Ga Rilwanulla Mukthar Abbas da karin bayani a cikin rahotonsa.

Your browser doesn’t support HTML5

A Ghana 'Yan Fashi Da Makami Na Yiwa Biranen Accra Da Tema Barazana - 3' 55"