Sake Tsayawa Takarar Buhari Ba Za Ta Yi Tasiri Ba – Sule Lamido

Sule Lamido

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP ta yi watsi da ayyana sake yin takara da shugaba Mohammadu Buhari yayi.

Tsohon gwamnan jihar Jigawa Alhaji Sule Lamido, ya ce ayyana sake takarar shugabanci da shugaba Mohammadu Buhari ya yi ba lalle ne hakan yayi tasiri ba a fagen siyasar Najeriya.

A cewar tsohon gwamnan jam’iyyar PDP uwa ce ga APC idan aka yi la’akari da mutanen da suka gina jam’iyyar. Kuma taron jam’iyyar PDP da aka yi a jihohi irin Jigawa da Katsina da kuma Sokoto shine ya firgita ‘yan jam’iyyar APC.

A bangarenta jam’iyyar APC mai mulki tace ita kam ko a jikinta don bata ganin PDP amatsayin barazana.

Sakataren APC na ‘kasa Mai Mala Buni, ya ce babu wata barazana da PDP zata iya yiwa APC, lokaci ne kawai zai yi halinsa.

Amincewar da shugaba Buhari yayi na sake tsayawa takarar zabe itace bukatar jam’iyyar APC a cewar Mai Mala Buni.

Tun bayan da shugaba Buhari yayi shelar sake yin takarar shugabancin Najeriya, manyan ‘yan siyasa musamman a Abuja ke ta tuntubar juna tsakanin masu mulki da masu adawa tun kafin a kada gangar siyasa gadan-gadan.

Domin karin bayani saurari rahotan Hassan Maina Kaina.

Your browser doesn’t support HTML5

Sake Tsayawa Takarar Buhari Ba Zai Yi Tasiri Ba – Sule Lamido - 2'05"