Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu Ya Yi Jimamin Rasuwar Asagba Mai Martaba Sarki Obi Joseph Chike Edozien


Asagba na Asaba, Mai Martaba Sarki, Obi Joseph Chike Edozien (CFR)
Asagba na Asaba, Mai Martaba Sarki, Obi Joseph Chike Edozien (CFR)

Shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu ya yi ta’aziyar rasuwar Asagba na Asaba, Mai Martaba Sarki, Obi Joseph Chike Edozien (CFR) wanda shine Asagba na 13 na garin Asaba dake Jihar Delta, ya kuma cika ne a ranar Laraba.

WASHINGTON, D. C. - A wata sanarwa da mai magana da yawun Tinubu, Ajuri Ngelale, ya fitar, ya jajantawa iyalan marigayin, Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Delta, da gwamnati, da kuma al’ummar jihar baki daya.

Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu
Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu

Shugaban ya kuma yi murna da irin tasirin rayuwar marigayin, wanda kuma fitaccen farfesa ne a fannin likitanci, tare da amincewa da irin shawarwarinsa na zaman lafiya a tsakanin 'yan Najeriya da kuma rawar da ya taka wajen neman kulla kawance a tsakanin ‘yan kasar mai makon rarrabuwar kawuna.

“Mai martaba ya yi cikakken rayuwa da aka ayyana ta mai girman akidar zaman lafiya, hadin kai, kishin kasa, gaskiya, da mutunci. Wannan babban rashi ne, yana zuwa a daidai lokacin da Najeriya ke bukatar karin masu samar da zaman lafiya da gina kasa,” in ji Tinubu.

Ya bukaci Iyalan sarkin da duk wadanda ke bakin cikin wannan rashi da su jajanta da irin tasirin da Mai Martaba Sarki ya bari.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG