Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sojoji 7 Sun Rasa Rayukansu A Chadi Sakamakon Fashewar Bam


Shugaban rukon kwarya na Chadi - Mahamat Deby
Shugaban rukon kwarya na Chadi - Mahamat Deby

Akalla sojoji bakwai ne suka rasa rayyukansu yayin da wani bam ya tashi a Chadi a yayin da suke sintiri a yammacin kasar kusa da tafkin Chadi, in ji gwamnatin kasar.

WASHINGTON, D. C. - Shugaban rikon kwarya, Mahamat Deby Itno, ya sanar da mutuwar sojojin a ranar Litinin a shafukan sada zumunta. Hukumomin kasar Chadi sun ce suna zargin mayakan Boko Haram daga Najeriya ne suka kai harin, lamarin da ke kara nuna damuwa game da karuwar tashe-tashen hankula a kusa da kan iyakar.

Kungiyar Boko Haram ta kaddamar da ayyukan ta’addanci fiye da shekaru goma da suka gabata kan ilimin boko tare da neman kafa shari'ar Musulunci a arewa maso gabashin Najeriya.

Rikicin ya bazu zuwa kasashen yammacin Afirka da suka hada da Kamaru, Nijar da kuma Chadi. Sama da mutane 36,000 ne aka kashe musamman a Najeriya a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

Deby Itno ya kwace mulki ne bayan da aka kashe mahaifinsa, wanda ya mulki kasar sama da shekaru 30, yana yakar 'yan tawaye a shekarar 2021.

-AP

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG