Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Buhari ya gana da wasu iyayen 'yan matan Chibok


Wasu iyayen matan da lungiyar Boko Haram ta sace
Wasu iyayen matan da lungiyar Boko Haram ta sace

Bayan kwanaki dari shida da sacesu wasu iyayen 'yan matan Chibok da har yanzu ke hannun 'yan Boko Haram sun gana da shugaba Buhari tare da kungiyar rajin ganin an sakosu

Kungiyar dake fafutikan ganin a sako 'yan matan Chibok da wasu cikin iyayen 'yan matan sun gana da shugaban kasa Muhammad Buhari.

A wurin ganawar da shugaban kasa ya basu tabbacin yana kwana yana tashi da damuwar 'yan matan a zuciyarsa tare da basu tabbacin cewa yana iyakar kokarinsa a sako yaran.

Shugaban ya fito fili ya fada bai san inda 'yan matan suke ba. Yac e shi ba zai yi karya ba domin ya farantawa kowa rai. Amma duk inda suke mayakan kasa da na ruwa da na sama suna shirye su je su kubutar dasu.

Shugaban ya bada umurnin a kafa kwamiti ya binciki yadda ma aka yi har ka asace yaran saboda wasu iyayen sun fadawa shugaban kasa a kebe cewa sun san wasu dake da hannu a sace 'ya'yansu.

Ga karin bayani

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:54 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG