Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Isra’ila Ta Zafafa Hare-Harenta Ta Sama A Lebanon, Tare Da Hallaka Fiye Da Mutane 180


APTOPIX Lebanon Israel
APTOPIX Lebanon Israel

A yau Litinin Isra’ila ta kaiwa wuraren Hizbullahi fiye da 100 hari ta sama, al’amarin da hukumomin lafiyar Lebanon suka ce ya hallaka akalla mutane 182, inda ta kasance rana mafi muni a kasar a rikicin da kungiyar dake samun goyon bayan kasar Iran ta shafe kusan shekara guda tana yi.

Bayan wasu daga cikin mafi munin musayar wuta akan iyakokin kasashen 2, Isra’ila ta gargadi jama’a su kauracewa wuraren da tace kungiyar mai gwagwarmaya da makamai ke boye makaman nata.

Lebanon-Israel border, on September 23, 2024.
Lebanon-Israel border, on September 23, 2024.

Bayan kusan shekara guda da kaddamar da yaki akan kungiyar Hamas ta zirrin Gaza dake iyakarta ta kudu, Isra’ila ta fara juya akalarta zuwa iyakarta ta arewa, daga inda kungiyar Hizbullahi ke kai harba mata makaman roka domin taimakawa kawarta hamas.

Lebanon-Israel
Lebanon-Israel

“Wannan mataki zai cigaba har sai mun cimma burinmu na mayar da mazauna yankin arewacin kasarmu gida cikin lumana,” a cewar Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant a bidiyon da ofishinsa ya wallafa, abinda ya shata fagen rikici mai dogon zango kasancewar hizbullahi ta sha alwashin cigaba da yaki har sai an tsagaita wuta a zirrin Gaza.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG