Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Juyin Mulki A Gabon


Olivier Veran
Olivier Veran

Faransa ta yi Allah wadai da juyin mulkin da aka yi a Gabon, ta kuma yi kira da a mutunta sakamakon zaben kasar da aka gudanar a makon da ya gabata, kakakin gwamnatin kasar Olivier Veran ya fada a ranar Laraba 30 ga watan Agusta.

WASHINGTON, D.C - Jami’an soji a kasar Gabon mai arzikin man fetur sun ce sun kwace mulki a ranar Laraba 30 da watan Agusta.

AFR-GEN GABÓN- Sojojin Da Suka Yi Juyin Mulki A Kasar Gabon
AFR-GEN GABÓN- Sojojin Da Suka Yi Juyin Mulki A Kasar Gabon

Sun kuma sanar da tsare Shugaba Ali Bongo, bayan da hukumar zaben kasar da ke tsakiyar Afirka ta sanar da cewa ya sake lashe wa’adi na uku.

A ranar Asabar aka gudanar da zaben shugaban kasa a kasar wanda sakamakonsa ke cike da korafe-korafe.

A cikin sanarwar da aka yi ta gidan talabijin da tsakar dare, wasu manyan jami’an soji 12 sun bayyana cewa an soke sakamakon zaben.

Sojojin sun kuma sanar da rufe kan iyakokin kasar da kuma rusa duk wasu cibiyoyin gwamnati.

Shugabannin juyin mulkin sun ce sun dauki wannan mataki ne da yawun dukkan hukumomin tsaron kasar.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG