Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Zabi Dan Najeriya Domin Fafatawa Wajen Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana


FBL-CAN-2024-NGR-ANG
FBL-CAN-2024-NGR-ANG

An zabi dan wasan gaban Super Eagles, Ademola Lookman, domin fafata wajen lashe kyautar dan kwallon kafa mafi bajinta a bangaren maza ta bana mai lakabin ballon d’or.

Sunan dan wasan mai shekaru 26 dake taka leda a kungiyar Atlanta ta kasar Italiya ya fito cikin jerin sunayen ‘yan wasa 29 da zasu fafata wajen lashe kyautar da mujallar kwallon kafar kasar Faransa ta wallafa a jiya Laraba.

Lookman ne dan wasa daya tilo daga nahiyar Afirka dake cikin jerin sunayen.

Ba’a sanya sunan dan wasan daya taba lashe kyautar har sau 8 kuma har yanzu yake rike da kabunta Lionel Messi a cikin jerin sunayen na bana ba, haka shima wanda ya taba lasheta har sau 5 Cristiano Ronaldo

Lookman na cikin karsashi kasancewar kungiyarsa ta atalanta ta lashe kofinta na farko a gasar nahiyar turai a kakar data gabata, inda dan najeriyar ya dura kwallaye 3 rigis a wasan karshe na gasar europa a ragar bayer leverkusen.

Ya ciwa atalanta jumlar kwallaye 17 tare da taimakawa a ci 11 a kakar da ta gabata.

wasu daga cikin fitattun ‘yan wasan dake cikin jerin sunayen sun hada da Jude Bellingham da Vini Junior da Erling Haaland da kuma Kylian Mbappe.

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG