Hukumar Kwastan reshen tashan jiragen ruwa ta Tin Can ta kama wasu tarin makamai da kayan soji da alburusai da kuma muggan kwayoyi da aka yi yunkurin shigowa dasu Najeriya ta hanyan sumogal.
Mambobin Kungiyar Kwadago ta Najeriya wato NLC sun gudanar da zanga-zanga a fadin kasar sakamakon matsin rayuwa, yunwa da tabarbarewar tattalin arziki a kasar.
Masana tattalin arziki a Najeriya na ganin matakan da gwamnatin kasar ke dauka da kyar za su yi tasiri, idan dai ba an kawo karshen matsalar tsaro da kuma dawo da tallafin man fetur da bude iyakoki domin shigowa da abinci cikin kasar ba.
Masu garkuwa da mutane sun bukaci a biya Naira miliyan 200 kudin fansa domin sako shugaban PDP na Legas da suka sace.
Sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken ya hallarci wani taro da bankin raya Afurka ya shirya a birni Legas na samar da abinci da kuma tallafa wa manoman nahiyar.
Shugaban Kasar Najeriya Bola Tinubu ya nuna alhininsa bisa rasuwar Sheikh Abdul-Hafeez Aṣhamu Abou, Baba Adinni na Legas, wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Zartarwa na Babban Masallacin Legas.
Gwamantin Najeriya tasha alwashin cigaba da nemo wasu hanyoyin samun kudaden shiga domin bunkasa tattalin arzikin kasar, maimakon dogaro da man fetur.
Domin Kari