‘Yau Ake Dakon Isowar ‘Yan Najeriyan Da Aka Kwaso Daga Sudan-NIDCOM

Shugabar hukumar NIDCOM, Abike Dabiri-Erewa

bayan kwashe kwanaki akan iyakar kasar Masar, ana sa ran cewa 'yan Najeriyan da aka ceto daga Sudan zasu iso gida Najeriya.

Shugabar hukuma mai kula da al’amuran ‘yan Najeira dake kasashen waje Abike Dabiri-Erewa ta bayyana cewa ‘Yan Najeriyan da aka kwaso daga Sudan zasu sauka a tashi da saukar jiragen sama na Nnamdi Azikiwe dake Abuja.

Abike Dabiri ta bada wannan sanarwar ne ta wani sakon da ta wallafa a shafinta na twitter a jiya Laraba tace ‘yan Najeiyan da aka kwaso daga Sudan sun baro kasar Masar a cikin wani jirgin sojin saman Najeriya kuma ana sa ran zasu isa tashar jirgin da misalign karfe 11: 23 na daren jiya.

Sakon da ta rubuta a shafin nata yace “A karshe dai, sun kamo hanyar zuwa gida cikin jirgin sojin saman Najeriya mai lamba C-130H wanda ya tashi daga Aswan kuma ana sa ran zasu isa babbar tashar jiragen saman Najeriya na Nnamdi Azikiwe dake birnin Abuja da misalign karfe 11:23 na daren yau” Muna Addu’a Allah Ya kawo su lafiya”.

Idan ba’a manta ba, shugabar ta NIDCOM a ranar asabar, ta sanar da cewa ofishin jakadancin Najeriya a Masar yana shirye-shiryen biyan kudaden bisan ‘yan Najeriyan da suka makale akan iyyakar kasar.