Matsayin Gwamnoni Kan Albashi: NLC, da PDP da APC Sun Mai Da Martani

  • Ibrahim Garba

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari

An shiga turka-turka saboda albashi. Yayin da gwamnonin jahohi ke kare aniyarsu ta kin biyan Naira dubu 18 a matsayin albashi mafi karanci, su kuma kungiyoyin NLC da PDP da APC cewa su ke hakan zai saba ma doka.

Kungiyar Kwadagon Najeriya (NLC) ta fito karara ta na kalubalantar duk wani gwamnan jaha da ya ce ba zai iya biyan Naira dubu 18 a matsayin mafi karancin albashi ba.

Wannan matsayin na kungiyar kwadago na samun goyon bayan wasu ‘yan siyasa, wadanda ke cewa matsayin na gwamnoni jahohi cike yak e da rashin tausayi da aldalci.

Mataimakin Sakatare-Janar na kungiyar ta NLC, Kwamrad Nuhu Toro ya ce doka ce ta tanaji biyan Naira dubu 18 a matsayin mafi karanci na albashin don haka wajibi ne a kalubalanci matsayin gwamnonin.

Ga wakilnmu na Bauchi Abdulwahab Muhammad da cikakken rahoton:

Your browser doesn’t support HTML5

Matsayin Gwamnoni Kan Albashi: NLC, da PDP da APC Sun Mai Da Martani - 3'14''