An Sake Kai Hari a Garin Kukawa a Jihar Borno

  • Ladan Ayawa
Wannan karon kuma da musalin karfe biyar da rabi na marance ne

Rahotanni dake fitowa daga karamar hukumar Kukakawa a jihar Borno na nuni da cewa wasu mahara da ake kyautata yayan kungiyar boko haram sun kai hari a garin ranar asabar da marance inda akace sun hallaka mutane da dama.

Sailin nan suka sa wa garin wuta wannan harin dai shine karo na biyu cikin makonni biyu da aka kai ga mazauna wannan garin na kukawa wanda a cikin makonni biyun ne ma jamaa suka afkawa jamaan dake garin dai lokacin da suke gudanar da sallar magriba wanda akace sun hallaka mutane 113.

Wannan karon kuma da musalin karfe biyar da rabi na marance ne dai wadannan mahara suka sake afkawa wa mazauna wannan gari wanda akace sunyi ma wasu yankan rago, sailin nan suka sa bindiga suka bibbidige wasu, kuma suka sawa gidajen mutane wuta.

Ga dai abinda wani mazauni garin da ya samu ya tsere yake cewa a hirar su da Haruna Dauda Biu.

‘’Da yamma boko haram sunzo garin kukawa’’

Jiya ne koyau?

‘’Jiya-jiya da yamma kamar karfe biyar’’

Ga dai Haruna Dauda Biu da ci gaban rahoton.

Your browser doesn’t support HTML5

Kukawa a jihar Borno - 2'39"