Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

‘Yan Sandan Pakistan Sun Kama Masu Zanga-zanga Da Dama A Karachi


'Yan sanda A Karachi Sun Kai Hari Kan Masu Zanga-zanga
'Yan sanda A Karachi Sun Kai Hari Kan Masu Zanga-zanga

Jam’iyyar ta ce daya daga cikin mambobinta ya mutu a rikicin.

‘Yan sanda a kasar Pakista sun harba hayaki mai sa hawaye tare da amfani da kulake a kan dubban masu zanga-zanga ranar Lahadi a birnin Karachi bayan masu zanga-zangar sun karya shingen jami’an tsaro.

Magoya bayan jam’iyyar masu ra’ayin rikau ta Islamist kusan 2,000 ne suka yi kokarin isa gidan jaridar birnin don nuna adawa da wata zanga-zangar da kungiyoyin farar hula suka yi game da kisan wani da ake zargi da aikata sabo a lokacin da yake tsare.

Magoya bayan jam’iyyar Tehreek-e-Lababaika Pakistan wato TLP sun yi ta jifa da duwatsu kan jami’ai tare da kona wata motar sintiri a lokacin da ‘yan sanda suka hana su isa gidan manema labarai.

Jam’iyyar ta ce daya daga cikin mambobinta ya mutu a rikicin. ‘Yan sanda sun kama mutane kusan 20 daga cikin zanga-zangar biyu.

Ministan Harkokin Cikin Gida na Yankin Zia Ul Hassan ya ce hukumomi na fargabar barkewar rikicin saboda jam’iyun siyasar biyu da kungiyoyin fararen hula sun yi kira da a gudanar da zanga-zanga a ranar guda.

Dandalin Mu Tattauna

TASKAR VOA: Yadda Tsofaffi Ke Fama Da Lalular Yanar Ido A Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Fim Da Aka Shirya Kan Leah Sharibu Ya Samu Lambar Yabo
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

TASKAR VOA: Kalubalen Da Masu Fama Da Lalurar Galhanga Ke Fuskanta
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Tasirin Cibiyar Kula Da Lafiyar Mata Da Yara Ta HopeXchange A Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:41 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG