Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

'Yan Sanda A Kenya Sun Yi Arangama Da Masu Zanga-zanga Kwana Guda Bayan Janye Kudurin Haraji


Masu zanga-zanga a Nairobi, Kenya
Masu zanga-zanga a Nairobi, Kenya

'Yan sandan Kenya sun harba barkonon tsohuwa kan masu zanga-zanga da dama tare da toshe titunan hanyar zuwa fadar shugaban kasar a ranar Alhamis, yayin da ake ci gaba da gudanar da kananan zanga-zanga a garuruwa da dama.

Zanga-zangar na ci gaba ne dai duk da cewa shugaban kasar ya janye kudirin karin harajin.

KENYA
KENYA

Adadin mutanen da suka fito yin zanga-zangar ya ragu sosai idan aka kwatanta da yawan mutanen da suka fito a baya-baya nan. Shugaba William Ruto ya janye dokar ne a ranar Larabar da ta gabata, kwana guda bayan arangamar da ta yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 23, inda kuma aka kai wa majalisar dokokin kasar hari na ‘dan gajeren lokaci tare da cinna wuta.

Ruto dai na fama ne da rikici mafi muni da bai taba gani ba a shugabancinsa na tsawon shekaru biyu a daidai lokacin da kungiyar masu zanga-zangar da matasa ke jagoranta ke karuwa cikin sauri sunna Allah wadai da karin harajin da aka yi a yanar gizo zuwa gangamin neman sauyi na siyasa.

Shugaban kasar Kenya William Ruto
Shugaban kasar Kenya William Ruto

Sakamakon rashin tsarin shugabanci na gari, masu zanga-zangar sun rabu kan yadda za a gudanar da zanga-zangar.

"Kada mu zama masu wauta yayin da muke fafutukar samar da ingantacciyar kasar Kenya," in ji Boniface Mwangi, wani fitaccen mai fafutukar tabbatar da adalci, a wani sakon da ya wallafa a shafin Instagram.

Kenya
Kenya

Ya bayyana goyon bayansa ga zanga-zangar a ranar Alhamis amma ya nuna adawa da kiraye-kirayen kutsawa kan gidan gwamnati, da ofisoshin shugaban kasa da kuma gidansa, matakin da ya ce zai iya haifar da mummunan tashin hankali da kuma amfani da hakan wajen ganin an murkushe su.

A Nairobi babban birnin kasar dai, 'yan sanda da sojoji sun yi sintiri a kan tituna ranar Alhamis tare da toshe hanyar shiga fadar gwamnati. 'Yan sanda sun kuma harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa mutane goma sha biyu da suka taru a tsakiyar birnin.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG