Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

NFF Ta Amince Eguavoen Ya Ci Gaba Da Horar Da Super Eagles


Augustine Eguavoen (Hoto: Facebook/Super Eagles)
Augustine Eguavoen (Hoto: Facebook/Super Eagles)

A daren Alhamis hukumar kwallon kafar ta NFF ta fitar da wannan sanarwar.

Kwamitin Zartarwa na Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya a ranar Alhamis ya amince da shawarar da kwamitin Kwararru da Ci gaba ya gabatar, kan mai horar wa Augustine Eguavoen ya ci gaba da jagorantar Super Eagles a matsayin Koci,

A daren Alhamis hukumar kwallon kafar ta NFF ta fitar da wannan sanarwar.

Kwamitin har ila yau ya ba da shawarar cewa Eguavoen ya ci gaba da jagoranci tawagar a wasannin neman shiga gasar cin Kofin Nahiyar Afirka ta 2025 da za su fafata da Libiya a ranar 11 ga watan Oktoba.

Eguavoen, mai shekara 58, wanda ke rike da tawagar na wucin gadi, bayan ya jagorance su sau uku a baya, ya jagoranci zakarun Afirka sau uku zuwa nasara da ci 3-0 kan Benin da kuma kunnen doki ba ci da Rwanda a wasannin ranar farko da ta biyu a farkon watan Satumba

Eguavoen da tawagar fasaha mai ci yanzu, wadda ta haɗa da Fidelis Ilechukwu, Daniel Ogunmodede, Olatunji Baruwa da Tomaz Zorec, za su kuma jagoranci tawagar Super Eagles B a wasannin neman cancantar shiga gasar cin Kofin CHAN na shekara mai zuwa.

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG