Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya: Matasa Sun Fara Zanga Zanga Kan Tsadar Rayuwa


An Fara Zanga-zangar Tsadar Rayuwa A Fadin Najeriya
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:16 0:00

An Fara Zanga-zangar Tsadar Rayuwa A Fadin Najeriya

Matasa a sassan Najeriya sun fara gudanar da zanga zanga kan tsadar rayuwa da sauran matsaloli da suke addabar kasar.

Matasan dai sun fito a kan manyan titunan biranan kasar, kama da Legas, Kano, Abuja, Borno da sauran su.

'Yan sandan Najeriya lokacin Zanga-zangar tsadar rayuwa
'Yan sandan Najeriya lokacin Zanga-zangar tsadar rayuwa

Matasan dai suna kokawa kan tsadar man fetur, wutar lantarki, kayan masarufi da dai sauran su, inda suke ta kiraye-kiraye da gwamnatin ta dauki matakai na kawo mafita daga wannan mawuyacin hali da al’ummar kasar take fuskanta na fatara da talauci.

Gwamantin tarayyar kasar ta nemi matasan da su kara ba ta lokaci domin tuni ta fara daukan matakai don magance wadannan matsaloli.

Matasa masu zanga-zangar tsadar rayuwa a Najeriya
Matasa masu zanga-zangar tsadar rayuwa a Najeriya

Sai dai matasan sun ce manufofin gwamnatin shugaba Bola Tinubu ne da ta dauka suka kara jefa kasar cikin wannan hali na matsi.

Tun a ranar 29 ga watan Mayu 2023 ne dai Tinubu ya ayyana cire tallafin man fetur da daidaita farashin canjin dalar Amurka.

Amma gwamnatin tarayyar ta ce manufofinta sun fara aiki, don haka mutane su kara hakuri kafin komai ya kankama.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG