Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ku Baiwa Gwamnati Karin Lokaci Ta Biya Bukatunku - Majalisar Dattawa


Zauren majalisar dattawan Najeriya (Facebook/Nigerian Senate)
Zauren majalisar dattawan Najeriya (Facebook/Nigerian Senate)

Rokon na zuwa ne bayan da Majalisar Dattawan ta sake hallara bayan wata ganawar sirrin da ta shafe kusan sa’o’i biyu a yau Laraba.

Majalisar Dattawan Najeriya ta roki masu zanga-zanga su baiwa gwamnatin tarayya karin lokaci domin sauye-sauyen da take gabatarwa su haifar da da mai ido tare da biyan bukatunsu.

Shugaban Makalisar Dattawan, Sanata Godswill Akpabio ya bayyana cewa gwamnatin ta fara biyan bukatun masu zanga-zangar ciki har da batun mafi karancin albashi da na rancen karatu ga dalibai da sayarwa matatu da danyen mai.

Ya cigaba da cewa, a shirye majalisar take ta yi dokoki a kan batutuwan da zasu kawowa ‘yan Najeriya saukin rayuwa.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG