Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mutane 22 Sun Mutu Sakamakon Tashin Gobara A Kamfanin Kera Batir A Koriya Ta Kudu


Masu kashe gobara a kamfanin batir na Hwaseong a Korea ta Kudu Yuni 24, 2024.
Masu kashe gobara a kamfanin batir na Hwaseong a Korea ta Kudu Yuni 24, 2024.

Wasu fashe-fashe sun yi sanadin tashin gobara a wata masana'anta ta batirin lithium a Koriya ta Kudu a ranar Litinin, inda suka kashe ma'aikata 22, mafi yawansu 'yan kasar China, yayin da kamfanin ya kone kurmus.

Gobarar ta tashi ne a wata masana'anta da ke karkashin masana'antar batir na Aricell a Hwaseong, wani rukunin masana'antu da ke kudu maso yammacin Seoul babban birnin kasar. Amma daga ƙarshe an kashe wutar gaba daya.

Ma'aikata 18 na kasar Sin da kuma ‘dan kasar Lao daya na cikin wadanda suka mutu.

Har yanzu ba a tabbatar da asalin ma’aikaciyar da ta mutu ba, kamar yadda jami’in kashe gobara Kim Jin-young ya shaida wa manema labarai.

Hwaseong
Hwaseong

Kim ya ce gobarar ta tashi ne da karfe 10:31 na safe (0131 GMT) bayan da wasu nau'ikan batir suka fashe a cikin wani dakin ajiyar kaya dauke da batir guda 35,000, in ji Kim, inda ya kara da yace ba a san abin da ya haddasa fashewar ba.

Wani ‘dan jaridar Reuters ya ga ma'aikatan kashe gobara sun kwashe gawarwaki shida daga cikin masana'antar. Saboda tsananin gobarar, masu aikin ceto sun samu wahalar gano wadanda suka mutu, in ji Kim.

Korea ta Kudu
Korea ta Kudu

Shugaban kasar Yoon Suk Yeol ya ziyarci wurin da hatsarin ya afku daga baya a ranar Litinin. Ministan cikin gida Lee Sang-min ya yi kira ga hukumomin yankin da su dauki matakin hana duk wani sinadari mai hatsarin gurbata muhallin da ke kewaye.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG