Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wasu Masu Ruwa Da Tsaki  Sun Ce Batun Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Salo Ne Na Raba Najeriya


Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Kano Najeriya Sun Gudanar Da Gangamin Wayar Da Kan 'Yan Bangar Siyasa
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:35 0:00

Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Kanon Najeriya Sun Gudanar Da Gangamin Wayar Da Kan 'Yan Bangar Siyasa

Masu ruwa da tsaki da suka hada da wakilan al’umma, masu fashin baki kan al’amuran yau da kullum da lauyoyi sun bayyana cewa, har yanzu Najeriya ba ta kai ga lokacin kafa ‘yan sandan jihohi ba la’akari da yadda ake zargin gwamnonin jihohi da juya kwamishinonin ‘yan sanda a jihohinsu.

ABUJA, NIGERIA - Hakan na zuwa ne kasa da kwanaki 10 da majalisun tarayyar Najeriya suka sanar da cewa majalisun jihohi 11 ne kawai suka amince da kudurorin gyare-gyare a kundin tsarin mulkin kasar bayan watanni 6 da aika musu don neman amincewarsu.

‘Yan majalisun tarayya da na jihohi, masu bibiyar al’amuran yau da kullum, iyaye mata da ma lauyoyi sun bayyana hakan ne a yayin taron zuren VOA da ya gudana a birnin tarayya Abuja suna masu cewa ganin yadda Najeriya ba ta gama tsayuwa a kan tsarin mulkin dimokuradiyya ba ta yadda za a ce lokaci ya yi na kafa ‘yan sandan jihohi, kamata ya yi a guje wa abun da ka je ya dawo.

Mahalarta taron dai sun yi ta bayyana rashin jin dadinsu a kan yadda majalisun jihohi 25 suka ki daukar mataki a kan gyare-gyaren da kwamitin majalisun tarayya suka tura musu a watanni 6 da suka gabata inda suka gindaya wasu sharudda kamar bukatar a sanya batun kafa ‘yan sandan jihohi a matsayın wajibci.

Aliyu Sabi Abdullahi, sanata mai wakiltar mazabar jihar Neja ta arewa a tarayyar Najeriya, ya bayyana cewa kusan kullum al’umma na bukatar a yi musu bayani a kan abubuwan dake tafe a kasa tare da cewa ana bukatar kafa ‘yan sandan jihohi sai dai lokacin hakan bai yi ba.

A nasa bangare, fitaccen lauya barista Mainasara Kogo ya yaba da kokarin ‘yan majalisun tarayya a game da aikin gyara kundin tsarin mulkin kasar, saidai baya ga hakan ya soke su a game da mayar da batun gyarar kundin tsarin mulkin kamar wata al’ada a kowanne zauren majalisa suna fito da zunzurutun kudi kuma daga karshe ba tare da yin nasara a gyarar da ya kamata a yi ba.

Idan Ana iya tunawa, kwamitocin majlisun tarayyar Najeriya da suka duba batun gyara kundin tsarin mulkin sun mikawa majalisun jihohin kasar 36 takardar gyare-gyaren ne a watannin 6 da suka gabata don samun amincewarsu kafin sanar da cewa jihohi 11 kawai ne suka jefa kuri’a a kan batun gyarar.

Jihohi 11 da suka dauki mataki a kan batun yin gyara a kundin tsarin mulkin dai sun hada da Abia, Akwa-Ibom, Anambra, Delta, Edo, Kaduna, Katsina, Kogi, Legas, Ogun da Osun kamar yadda mataimakin shugaban majalisar dattawa kuma shugaban kwamitocin majalisun, Sanata Ovie Omo-Agege, ya bayyana.

Saurari cikakken rahoto daga Halima Abdulrauf:

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Ce Batun Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Salo Ne Na Raba Najeriya.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:24 0:00

XS
SM
MD
LG