Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Na’am da Kafa Rundunar G5 Sahel


Sojojin kasar Mali suna atisaye
Sojojin kasar Mali suna atisaye

Kwamitin tsaro na majlaisar dinkin duniya ya yi na’am da shawarar da kasashen yankin SAHEL suka gabatar ta hanyar kungiyar hadin kan kasashen nahiyar Afrika- AU, domin kafa rundunar hadin guiwar G5 Sahel mai alhakin yakar ‘yan ta’adda akan iyakokin kasar Mali da makwaftanta.

Taron kwamitin tsaron da aka gudanar a birnin Nyame ne ya sanar da yin na’am da yunkurin da kasashe biyar na yankin Sahel suka sa gabatar domin murkushe kungiyoyin ta’addancin dake addabar kasar Mali da makwabta, ta hanyar kafa rundunar hadin guiwa ta G5 Sahel.

Ministan harkokin kasashen ketare na Jamhuriyar Nijar Alhaji Ibrahim Yakuba ya bayyana cewa, wannan zai kara karfin guiwa ga kasashen da kuma dukan wadanda suke son su taimaka masu domin ganin sun cimma nasara.

Ministan yace idan aka tara sojojin kimanin dubu biyar aka kuma dauki lokaci ana iya cimma nasara. Ya bayyana cewa, suna so su sami irin nasarar da aka cimma a Najeriya wajen karya lagon kungiyar, inda suke hankoron ganin sun hana ‘yan ta’adda kai hare hare a cikin Mali balle har su fita wadansu kasashen ketare.

Sai dai sharuddan da kwamitin tsaron na majalisar Dinkin Duniya ke aiki a karkashinsu suka gindaya, sun kawo cikas wajen ba kasashen na Burkina Faso, Mali, Nijar, Chadi da Mauritaniya cikakken goyon bayan da zai basu damar kai farmaki har can gindin magani.

Alhaji Ibrahim Yakuba ya bayyana cewa, sun so a basu damar su iya shiga har Mali ko kuma su isa kan iyaka da kasar su kai hari a cikin wani izini dake karkashin tsarin.

Ya bayyana cewa Kungiyar kasashen Tarayyar Turai ta ba rundunar hadin guiwar tallafin kimanin saifa miliyan talatin kwanakin baya, suna kuma neman sauran kasashen su bada nasu tallafi kasancewa matsala ce da ta shafi dukan kasashe .

Ga cikakken rahoton da wakilin Sashen Hausa Sule Mummuni Barma ya aiko daga birnin Nyame.

Kwamitin Tsaro ya yi na'am da kafa rundunar tsaro ta Sahel-2'55
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:56 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG