Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotu Ta Yi Sammacin Yahaya Bello


Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello
Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello

A cewar sammacin, tsohon gwamnan zai halarci zaman kotun na rana r 24 ga watan Oktoba domin amsa tuhume-tuhumen sannan zai gurfana ne tare da wasu mutane 2 da ake karar tare.

Mai Shari’a Maryanne Anenih ta babbar kotun tarayya ta Abuja ta mika sammancin da za a yada ga tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, a kan ya halarci zaman kotun domin amsa wasu ragowar tuhume-tuhume 16 da ake yi masa.

A cewar sammacin, tsohon gwamnan zai halarci zaman kotun na rana r 24 ga watan Oktoba domin amsa tuhume-tuhumen sannan zai gurfana ne tare da wasu mutane 2 da ake karar tare.

Mai Shari’a Anenih ta ba da umarnin sammacin da ake yadawa ne a hukuncin da ta zartar sakamakon bukatar da hukumar efcc mai yaki da almundahana a najeriya ta gabatar.

Mai Shari’a Anenih ta umarci EFCC ta wallafa sammacin a jarida mafi farin jini.

Haka kuma ta umarci EFCC ta kafe kwafin sammacin a tsohon adireshin da aka sani na Yahaya Bello da bayyanannun wurare a harabar kotun.

A ranar 24 ga watan Satumbar da ya gabata, EFCC ta yi ikrarin cewar ta kasa mika takardun tuhuma ga yahaya bello, inda aka tuhumi tsohon gwamnan da wasu mutane 2 da laifin cin amana ta kudaden da suka kai Naira biliyan 110.4.

Sauran mutane 2 da ake tuhuma sun hada da Umar Oricha da Abdulsalami Hudu.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG