Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yahaya Bello Ya Amsa Gayyatar EFCC


Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello
Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello

A yau Laraba aka ce tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya amsa gayyatar da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC ta yi masa.

A wata sanarwa da Daraktan ofishin yada labarai na Yahaya Bello, Ohiare Michael ya fitar a ranar Laraba, an tabbatar da cewa Bello ya yanke shawarar karrama wannan gayyata ne biyo bayan tattaunawa da ya yi da iyalansa, da kungiyar lauyoyi, da kuma abokan siyasa.

"Muna fatan hukumar za ta gudanar da aiki bisa kwarewa da kuma mutunta yancinsa a matsayin ɗan ƙasa," in ji sanarwar.

Tsohon gwamnan, wanda a baya an ayyana nemansa bisa zargin karkatar da kudade da sauran ayyukan almundahana da suka kai Naira biliyan 80.2.

Ya kuma samu rakiyar manyan ‘yan Najeriya zuwa ofishin hukumar.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG