Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar Kula Da Ayyukan ‘Yan Sandan Najeriya Ta Kori Wasu Manyan ‘Yan Sanda Bakwai, Ta Rage Mukaman Wasu


Hukumar Kula Da Ayyukan ‘Yan Sandan Najeriya Ta Kori Wasu Manyan ‘Yan Sanda Bakwai, Ta Kuma Rage Mukaman Wasu
Hukumar Kula Da Ayyukan ‘Yan Sandan Najeriya Ta Kori Wasu Manyan ‘Yan Sanda Bakwai, Ta Kuma Rage Mukaman Wasu

Hukumar dake kula da ayyukan yansandan Najeriya ta kori wasu manyan ‘yan sanda bakwai daga bakin aiki tare da rage mukaman wasu ‘yan sandan.

ABUJA, NIGERIA - Hukumar Kula da ayyukan ‘yan sandan Najeriyar, wacce ta shafe kwanaki tana gudanar da taronta karo na goma sha biyar a birnin Abuja, ta amince da korar wasu manyan Jami'an ‘yan sanda bakwai da kuma rage mukaman wasu manyan jami'ai goma.

Hukumar Kula Da Ayyukan ‘Yan Sandan Najeriya Ta Kori Wasu Manyan ‘Yan Sanda Bakwai, Ta Kuma Rage Mukaman Wasu
Hukumar Kula Da Ayyukan ‘Yan Sandan Najeriya Ta Kori Wasu Manyan ‘Yan Sanda Bakwai, Ta Kuma Rage Mukaman Wasu

Mai magana da yawun hukumar Ikechukwu Ani ya fada a wata sanarwar da ya sanya wa hanu cewa hukumar ta ja kunnen wasu ‘yan sanda goma sha uku kana za a bai wa wasu biyu kuma takardun gargadi yayin da ta wanke wasu guda hudu.

Hukumar dai ta dau wannan mataki ne a matsayin wani bangare na ladabtarwa akan jami'an da aka samu da wuce gona da iri wajen tafka laifi yayin gudanar da ayyukansu.

Hukumar Kula Da Ayyukan ‘Yan Sandan Najeriya Ta Kori Wasu Manyan ‘Yan Sanda Bakwai, Ta Kuma Rage Mukaman Wasu
Hukumar Kula Da Ayyukan ‘Yan Sandan Najeriya Ta Kori Wasu Manyan ‘Yan Sanda Bakwai, Ta Kuma Rage Mukaman Wasu

Wannan mataki dai tuni ya ja hankalin kwararru da masana tsaro irinsu Dr. Kabiru Adamu da ke ganin dacewar abin, inda ya ce akwai gibi sosai na rashin aminci tsakanin ‘yan sanda da jama'a fararen hula.

Shi ma mai sharhi akan al'amuran yau da kullum Dr. Farouk BB Farouk wanda ya yaba wa hukumar amma ya ce akwai bukatar nan gaba a bayyana sunayen jami'an da kuma irin laifin da suka yi.

Saurari cikakken rahoton daga Hassan Maina Kaina:

Hukumar Kula Da Ayyukan ‘Yan Sandan Najeriya Ta Kori Wasu Manyan ‘Yan Sanda Bakwai, Da Rage Mukami Wasu.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:58 0:00

XS
SM
MD
LG