Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GHANA: Ba Mu Goyi Bayan Shugaba Nana Akufo-Addo Wajen Tura Sojoji Ghana Zuwa Nijar Ba - Shugaban Jam'iyyar Adawa Ta GUM


Wasu daga cikin Rundunar Sojojin ECOWAS lokacin da suka je taron gaggawa na kwana biyu a Accra, Ghana
Wasu daga cikin Rundunar Sojojin ECOWAS lokacin da suka je taron gaggawa na kwana biyu a Accra, Ghana

Yayin da ECOWAS ta yanke shawara kan ranar da za ta aika dakarunta zuwa Nijar, bayan taron kwana biyu a  birnin Accra,  shugaban jam'iyyar adawa ta GUM, Rev. Christian Kwabena Andrews ya yi barazanar yin da zanga-zanga idan har Gwamnatin Ghana ta baiwa ECOWAS dakaru soja domin yaki a Nijar.

Reverend Christian Kwabena Andrews wanda aka fi sani da Osofo Kyiri Abosom, ya yi wannan kalaman ne a taron manema labarai a Accra.
"Mun zo nan ne don bada shawara da kuma sa hannu kan wannan takardan dangane da shugaban kasar Ghana Nana Addo Dankwa Akufo Addo da kada ya biye wa ECOWAS wajen tura Sojoji Ghana zuwa Niger. Baza mu goyi bayansa ba a matsayin mu 'yan kasar Ghana. Ina shaida wa Akuffo Addo da duk wani dan kasar Ghana cewa mu nisanci wannan shawara mara amfani da kungiyar ECOWAS ta dauka na tura sojojin mu zuwa Nijar. Kada wanda ya isa ya yi caca da rayukan sojojin mu. Kuma idan shugaban kasa ya ki saurarenmu sai wani abu ya faru, mu 'yan jami'iyyar GUM za mu fara zanga-zangar nuna kyama ga shugaban kasa da gwamnatinsa."

A gefe daya kuma Shugaban babban jam’iyyar adawa a Ghana (NDC), Johnson Asiedu Nketiah, ya gargadi shugaban kasar Nana Addo Dankwa Akufo-Addo game da tura sojojin Ghana zuwa Nijar, wadda take fama da juyin mulkin a halin da ake ciki yanzu.

Asiedu Nkatia ya ce zai gaya wa Shugaban Ghana Nana Akufo Addo da duk mutanin Ghana su kula, kada a dauki rayukar 'yan uwanmu sojoji a yi caca da su, a kan wannan matakin da bashi da amfani kwata-kwata.

Haka kuma mafi yawancin mutanen Ghana ba su da ra'ayin aika sojoji domin a yaki Nijar.

Mallam Adib Sani masanin tsaron da al'ammurra siyasar kasa da kasa ya ce duba da matsalolin tabarbarewar tattalin arziki da matsalolin tsaro da suka addabi kasashen yammacin Afrika, musamman Najeriya dake fama da Boko Haram da sauran kungiyoyin 'yan ta'adda da kuma matsalar rashin tsaron daga arewa maso gabashin Ghana, babu wani yaki da zai iya faruwa.

Saurari rahoton Hawawu Abdul Karim Young Pioneer:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:58 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG