Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Yi Fashin Jirgin Ruwan Mai A Dab Da Gabar Tekun Najeriya


Bakin gabar teku a Bombom, tsibirin Principe na Tarayyar Tsibiran Sao Tome da Orincipe mai kallon mashigin ruwan Guinea, dab da Najeriya, inda yanzu fashi cikin teku yake karuwa.
Bakin gabar teku a Bombom, tsibirin Principe na Tarayyar Tsibiran Sao Tome da Orincipe mai kallon mashigin ruwan Guinea, dab da Najeriya, inda yanzu fashi cikin teku yake karuwa.

An yi fashin jirgin ruwan na kasar Girka kilomita 55 daga gabar Najeriya lokacin da ya dauko man fetur daga kasar Ghana zuwa Jamhuriyar Benin

Jami’an kula da zirga-zirgar jiragen ruwa na kasar Girka sun ce ‘yan fashi sun cafke wani jirgin ruwan tanka na kasar a dab da gabar Najeriya.

Jami’ai sun fada yau litinin cewa a ranar asabar aka yi fashin jirgin dakon man fetur mai suna "Aegean Star" da ma’aikatansa su 20. Suka ce an yi fashin wannan tanka a cikin teku kimanin kilomita 55 daga gabar Najeriya a cikin mashigin ruwan Guinea, a lokacin da yake kan hanyar zuwa Jamhuriyar Benin dauke da mai daga kasar Ghana.

An ce ma’aikatan jirgin ruwan sun hada da Girkawa uku da wasu daga kasashe dabam-dabam. Har yanzu babu labarin halin da suke ciki.

Koda yake ba su yi kaurin suna kamar takwarorinsu na Somaliya ba, ‘yan fashi cikin teku su na kara zafafa ayyukansu a cikin mashigin ruwan Guinea. A watan da ya shige, Hukumar Kula da Zirga-Zirgar Jiragen Ruwa ta Duniya ta ja kunnen jiragen ruwa game da wucewa ta kusa da jamhuriyar Benin. Hukumar ta ce ‘yan fashi sun kwace jiragen ruwa da dama a wannan shekara, ciki har da wani jirgin ruwan tanka na Girka da aka yi fashinsa ranar 16 ga watan Yuni.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG