Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Dage Dokar Hana Fita a Jihar Tarba


Yanzu haka dai hankali ya kwanta a yankunan Taraba, bayan wani hargitsi mai nasaba da sakamakon zaben gwamna a jihar inda aka sami hasarar rayuka da kuma kone-kone a garin Gyambu.

Rahotanni sun nuna cewa bayan garin Gyambu an sami barkewar hatsaniya a wasu sassan jihar ta Taraba musamman a tsakanin magoya bayan dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar wato Architect Darius Ishaku da kuma magoya bayan ‘yar takarar jam’iyyar adawa ta APC sanata Aisha Jummai Alhassan da ake yi wa lakabi da Maman Taraba.

Sakamakon wannan hatsaniyar ne ya sa gwamnatin jihar kafa dokar hana fita tun daga karfe bakwai na maraice har zuwa karfe shida na safe.

ASP Joseph Kwaji ya tabbatar da cewa hankula sun kwanta bayan rigimar da ta kacame tsakanin ‘yan PDP da ‘yan APC ya kuma ce an baza 'yan sanda a yankunan.

‘Yan takarar kujerar gwamna da ‘yan jam’iyyunsu sun maida martani game da takaddamar soke zabe da sake shi a wasu yankuna da ake zargin an sace akwatunan zabe da kuma aringizon kuri’u.

Chief David Sabo Kente, dan takarar jam’iyyar SDP ya ce su kam sun yi na’am da batun sake zaben.

Shi kuma dan takarar jam’iyyar PDP Architech Darius, a ta bakin wani hadiminsa, ya fadi cewa ba a yi masu adalci ba.

A nata bangaren kuma, jam’iyyar adawa ta APC ta bayyana rashin jin dadinta bisa ga matakin da aka dauka a ta bakin shugabanta Malam Jika Ardo.

Inda ya ce duk da cewa hukumar zabe ke da hurumin daukar matakin kuma ba abin da za su yi, abin dai bai yi ma ‘yan jam’iyyar dadi ba saboda tun kafin zabe sun gabatar da koke-kokensu amma ba a saurare su ba.

Ga karin bayani daga Ibrahim Abdul’aziz.

An Dage Dokar Hana Fita a Jihar Taraba - 2'49"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:49 0:00

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG