Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Tarayya Da Kungiyoyin Kwadago Sun Amince Da N70, 000 A Matsayin Mafi Karancin Albashi


Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, a ranar Ma'aikata ta Duniya
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, a ranar Ma'aikata ta Duniya

Ministan yace an cimma wannan matsaya ne a yayin wata ganawa tsakanin Shugaban Najeriya, Bola Tinubu da shugabannin kungiyoyin kwadago na NLC da TUC a Abuja a yau Alhamis.

Ministan Yada Labarai Muhammad Idris, yace gwamnatin tarayya da shugabannin hadaddiyar kungiyar kwadago sun amince da naira dubu 70 a matsayin mafi karancin albashin ma’aikatan Najeriya.

“A yau Alhamis muna farin cikin sanar da cewa hadaddiyar kungiyar kwadago da gwamnatin tarayya sun amince da yin kari akan mafi karancin albashi na naira dubu 62. Don haka sabon mafi karancin albashin da ake sa ran mai girma shugaban kasa ya gabatarwa majalisar kasa shine naira dubu 70, “a cewar Muhammad Idris.

Yayin bada sanarwar ga manema labaran fadar shugaban kasa, an ga shugaban kungiyar kwadago ta NLC, Joe Ajaero da takwaransa na tuc, Festus Osifo tare da Ministar Kwadago, Nkiruka Onyejeocha da sauran jami’an gwamnati a kewaye da ministan.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG