Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zaben Edo: INEC Ta Mika Takardar Shaidar Cin Zabe Ga Okpebholo


Gwamnan jihar Edo mai jiran gado, Monday Okpebholo,
Gwamnan jihar Edo mai jiran gado, Monday Okpebholo,

Bikin mika takardar shaidar cin zaben ya gudana ne a shelkwatar INEC dake Abuja a yau Alhamis.

Hukumar zaben mai zaman kanta ta Najeriya (INEC) ta mika takardar shaidar cin zabe ga mutumin daya lashe zaben gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo, na jam’iyyar APC.

Bikin mika takardar shaidar cin zaben ya gudana ne a shelkwatar INEC dake Abuja a yau Alhamis.

INEC ta ayyana Okpebholo a matsayin wanda yayi nasara a zaben da ya gudanar a ranar Asabar, 21 ga watan Satumbar da muke ciki bayan samun kuri’u 291, 667 inda ya doke dan takarar dake biye da shi, Asue Ighodalo na jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 247, 274.

Dan takarar jam’iyyar APC ya samu galaba a fiye da kananan hukumomi 10 daga cikin 18, inda ya bar dan takarar da kwarya-kwaryar nasara a ragowar kananan hukumomin.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG