Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nijar: Kishin Ruwa Ya Kashe Bakin Haure 50 A Hamada


Safarar bakin haure
Safarar bakin haure

Kungiyoyin agaji dake aikin ceto akan iyakar Libiya da Nijar sun sanar da gano gawarwakin bakin haure da suka mutu a cikin hamadar Sahara wadanda alamu ke nuna cewa tsananin kishin ruwa ne yayi sanadin mutuwar su

Yankunan sahara Agadas wadanda suka raba iyakoki da kasashen Libiya da Aljeriya a arewacin Nijar sune su kafi zama mafi hatsarin ga bakin haure dake son shiga Turai

A yan kwanakin nan ana samun yawaitar bakin haure dake mutuwa a cikin hamadar sahara inda kungiyoyin agaji suka sanar da mutuwar bakin haure kusan 50 yayinda suka ceto akalla 200 da aka zubar dasu.

Tun bayan soke dokar haramta safarar bakin haure da gwamnatin mulkin sojin Nijar tayi a shekarar da ta gabata ake samun yawaitar mutuwar bakin haure dake bi ta barauniyar hanya wanda masu jigilar suke zubar dasu a cikin hamada, lamarin da ya sa kungiyar dake aikin jigilar bakin haure yin kira ga gwamnati ta dauki mataki

A saurari rahoton Hamid Mahmoud:

Ana Samun Yawaitar Mutuwar Bakin Haure A Hamadar Sahara
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:40 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG