Wata Fashewa Ta Hallaka Mutane 2 A Kasuwar Zamfara

Kano

Kano

Al’amarin daya faru a jiya Talata, ya haddasa tsananin fargaba inda ‘yan kasuwa da masu sayen kaya suka rika gudun neman tsira a kasuwar mai yawan hada-hada.

Fashewar da garin harsashin bindiga ya haddasa a kasuwar Talatar-Mafara dake jihar Zamfara, ta hallaka mutane 2.

Al’amarin daya faru a jiya Talata, ya haddasa tsananin fargaba inda ‘yan kasuwa da masu sayen kaya suka rika gudun neman tsira a kasuwar mai yawan hada-hada.

Wani ganau yace fashewar ta samo asali ne daga wani kanti da ake sayar da bindigogi kirar gida.

Shugaban karamar hukumar Talatar Mafara, Yahaya Yari, ya tabbatar da afkuwar lamarin a yau Laraba.

Ya kuma bayyana cewar an garzaya da mutanen da suka jikkata sakamakon fashewar zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Usman Danfodio dake Sokoto domin samun kulawa.