Wai Ina Makomar Sojojin Najeriya 59 da Aka Yankema Hukuncin Kisa?

Sojojin da ake zargi da kin zuwa Arewa maso gabacin kasar domin yakar masu tsassauran ra'ayin addini sun hallara a gaba kotun Soja a Abuja, 2 ga Oktoba 2014.

Wasu sojojin Najeriya da aka yanke ma hukuncin kisa.

Shin wai hukuncin da aka yanke ma sojojin Najeriya 59 na kisa bisa samun su da akayi da take hakin bil’adam yayi dai dai kuwa? Farfesa Abdullahi Zuru na jami'ar Abuja, ya kira wannan hukunci da sunan bita da kulli.

Ya nuna cewar babu inda akace idan kana shugaba kuma kai ne me kara kuma kazama maiyanke hukunci. Don akwai tabbacin bazakayi ma wanda ake zargi adalci ba, bisa ga wannan dalilin da ma wasu, wanda idan akayi irin wannan shari’ar a boye to wadanda akayi ma wannan shari’ar na da hurumin su daukaka kara zuwa kotun farar hula, don neman hakinsu. Kuma anyi irin wadannan shari’oin a Gwantanamo wanda shugaban kasar Amurika Barak Obama yabada umurni abasu damar neman hakinsu na ‘yan adam.

Yayi bayani cewar ana sa ran wannan hukunci zai iya chanzawa tunda yanzu muna mulkin demokradiyya ne, don haka akwai tunanin za su daukaka kara wanda babu mamaki idan aka samesu basu aikata abun da ake tuhumarsu da shiba to za’a iya sakinsu.

Your browser doesn’t support HTML5

Wai Ina Makomar Sojojin Najeriya 59 da Aka Yankema Hukuncin Kisa? - 3'07"