Majalisar Dokokin Ghana Ta Kada Kuri'ar Soke Hukuncin Kisa

Ghana

Majalisar Dokokin Ghana ta kada kuri'ar soke hukuncin kisa, wanda ya sa kasar ta kasance ta baya-bayan nan cikin jerin kasashen Afirka da dama da suka yi yunkurin soke hukuncin kisa a shekarun baya-bayan nan.

WASHINGTON, D.C. - Babu wanda aka yanke wa hukuncin kisa a Ghana tun shekarar 1993, ko da yake an yanke wa mutane 176 hukuncin kisa a bara, kamar yadda Hukumar kula da gidajen yari ta Ghana ta bayyana.

Sabon kudirin dokar dai zai yi kwaskwarima wa dokar sashen kundin mulkin kasar kan hukuncin kisa zuwa daurin rai da rai, a cewar rahoton kwamitin Majalisar.

Amma dai sai shugaban kasar Nana Akufo-Addo ya amince da dokar kafin ta fara aiki.

Nana Akufo Addo

"Wannan wani babban ci gaba ne na ayyukan kare hakkin bil'adama na Ghana," in ji Francis-Xavier Sosu, ‘dan Majalisar da ya gabatar da kudirin.

"Mun gudanar da bincike tun daga kan tsarin mulki har zuwa kuri'ar jin ra'ayin jama'a, kuma dukkansu sun nuna cewa yawancin 'yan Ghana na son a soke hukuncin kisa," kamar yadda Xavier Sosu ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

A yanzu Ghana ita ce kasa ta 29 da ta soke hukuncin kisa a Afirka kuma ta 124 a duniya, in ji ‘The Death Penalty Project,’ wata kungiya mai zaman kanta da ke London, wadda ta ce ta yi aiki tare da abokan hulda a Ghana don taimakawa wajen ganin an sauya dokar.

Kasashen Equatorial Guinea da Saliyo da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da kuma Zambia na daga cikin kasashen Afirka na baya-bayan nan da suka kawo karshen hukuncin kisa a cikin shekaru biyu da suka gabata.

-Reuters