Hanyoyin Diflomasiyya Da Ya Kamata Abi Don Warware Rikicin ECOWAS Da Mahukuntan Nijar – Ambasada Bala Sani

Hoton: ECOWAS

Batun takaddama tsakanin shugabannin kungiyar raya tattalin arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tnubu ke jagoranta da shugabannin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar na ci gaba da daukar hankalin masana da masu fashin bakin kan sha’anin siyasa da diflomasiyya.

Yanzu haka dai takunkumin da kungiyar ECOWAS din ta kakabawa Jamhuriyar Nijar na ci gaba da haifar da mummunan tasiri kan harkokin kasuwanci da sauran al’amuran tattalin arzikin kasar.

A watan Yulin da ya gabata ne sojoji suka hambarar da gwamnatin farar hula ta shugaba Mohammed Bazoum tare da tsare shi da iyalansa.

A wani taro na baya bayan nan da shugabannin Kungiyar ECOWAS suka gudanar a Abuja, sun gindaya wa mahukuntan Nijar din wasu sharuda kafin a dage wadannan takunkumai na karya tattalin arziki.

Sharudan sun hada da gaggauta sakin hambararren shugaban kasa Mohamed Bazoum da iyalinsa da ma dukkan mutanen da aka kama a sakamakon wannan al’amari, kafin a fara duba hanyoyin dage takunkumin da ka kakaba wa kasar.

A hirar su da wakilin mu na Kano Mahmud Ibrahim Kwari, Ambasada Bala Sani, tsohon Jakadan Najeriya a kasashen Jamus, Mouritaniya da kuma Ghana ya fayyace wasu daga cikin hanyoyin diflomasiyya da ka iya warware takaddamar.

Saurari cikakkiyar hira cikin sauti:

Your browser doesn’t support HTML5

Hanyoyin Diflomasiyya Da Ya Kamata Abi Don Warware Rikicin ECOWAS Da Mahukuntan Nijar – Ambasada Bala Sani.mp3