Garin Misau Hedkwatan Karamar Hukuma Bata da Ma'aikatar Kashe Gobara

Gobara tana ci.

Gobara ta kona wani mai yin aikin walda, agarin Misau dake jihar Bauchi.

Kawo yanzu garin Misau mai zama hedkwatan karamar hukumar bata da ma’aikatan kashe gobara a karamar hukumar, idan aka samu gobara saidai a kawo dauki daga Azare.

A yau gobara ta kona wani mai yin aikin walda, agarin Misau dake jihar Bauchi, sanan ta kona wasu mutane biyar, wandanda a halin yanzu suke kwance a asibitin garin Misau.

Gobaran ya faru ne a lokacin da mai aikin waldan ke kokarin toshe tankunar wasu motocin daukar mai a harabar ma’aikatan ruwa, a garin na Misau, inji shugaban karamar hukumar ta Misau, Alhaji Muhammad Kure Misau, ya kuma kara da cewa karamar hukumar zata dauki nauyin majiyatan.

Your browser doesn’t support HTML5

Garin Misau Hedkwatan Karamar Hukuma Bata da Ma'aikatar Kashe Gobara - 3'28"