Eden Hazard Ya Yi Ritaya Daga Bugawa Kasarsa Kwallo

Eden Hazard

Hazard ya bayyana hakan ne mako guda bayan da aka cire Belgium daga gasar cin kofin duniya da ke wakana a Qatar.

Dan wasan gaba na kasar Belgium Eden Hazard, ya yi ritaya daga bugawa kasar wasa.

Hazard ya bayyana hakan ne mako guda bayan da aka cire Belgium daga gasar cin kofin duniya da ke wakana a Qatar.

Dan shekara 31, Hazard ya fara takawa Belgium kwallo a shekarar 2008 a lokacin da dan shekara 17

Ya bugawa Belgium wasa 126 ya kuma ci kwallaye 33. Hazard ya bayyana ritaysar shi a shafin Instagram dinsa.

“Na yanke shawarar kawo karshen taka kwallo a matakin kasa da kasa.

“Lokacin da za a gaje mu ya zo. Zan yi kewar ku.” Hazard ya rubuta.