Dakta Aliyu Idi Hong ya ce Zabe Zai Yi Wuya a Jahohin da Ake Dokar ta Baci

Dr. Aliyu Idi Hong

Tsohon minista dakta Aliyu Idi Hong yayi furucin ne a tattaunawar su da Aliyu Mustaphan Sokoto na Muryar Amurka
Bayan furucin da furofesa Attahiru Jega yayi game da shirya zabe a jahohi uku na arewa maso gabashin Najeriya da ke cikin dokar ta baci, wato Yobe da Borno da Adamawa, shi ma tsohon ministan harakokin wajen Najeriya, tsohon ministan lafiya, kuma tsohon ministan yawon shakatawa da al'adu dakta Aliyu Idi Hong ya tofa albarkacin bakin shi akan shirya zaben a wadannan jahohi:

Your browser doesn’t support HTML5

Tsohon Minista dakta Aliyu Idi Hong a kan zaben a jahohin da ake dokar ta baci - 2:49


Dakta Aliyu Idi Hong yayi wannan bayani ne a tattaunwar su da babban editan Sashen Hausa na Muryar Amurka Aliyu Mustapahn Sokoto lokacin da ya kawo ziyara Muryar Amurka.

Babban Editan Sashen Hausa na Muryar Amurka Aliyu Mustaphan Sokoto